15
Annabci a kan Mowab
Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne,
An lalatar da Ar a Mowab,
an hallaka ta da dare!
An lalatar da Kir a Mowab,
an hallaka ta da dare!
Dibon ya haura zuwa haikalinta,
zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka;
Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba.
An aske kowane kai
an kuma yanke kowane gemu.
A tituna sun sa tsummoki a jikunansu;
a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa
dukansu sai makoki suke yi,
sun kwanta suna kuka.
Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi,
aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz.
Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi,
har zuciyarsu ta karai.
 
Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab;
mutanenta sun gudu har zuwa Zowar,
har zuwa Eglat Shelishiya.
Sun haura zuwa Luhit,
suna tafe suna kuka;
a kan hanyar zuwa Horonayim
suna makoki saboda hallakawarsu.
Ruwayen Nimrim sun ƙafe
ciyayin kuma sun bushe;
tsire-tsire duk sun ɓace
babu sauran ɗanyen abu.
Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye
sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab;
kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim,
makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
Ruwayen Dimon sun cika da jini,
amma zan yi ƙari a kan Dimon,
zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab
da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.