31
Kaiton waɗanda suke dogara ga Masar
Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako,
waɗanda suke dogara ga dawakai,
waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu
da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu,
amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila,
ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa;
ba ya janye kalmominsa.
Zai yi gāba da gidan mugu,
gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba;
dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba.
Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa,
shi da yake taimako zai yi tuntuɓe
shi da aka taimaka zai fāɗi;
dukansu biyu za su hallaka tare.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini,
“Kamar yadda zaki kan yi ruri
babban zaki a kan abin da ya yi farauta,
kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya
sun taru wuri ɗaya a kansa,
ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba
ko ya damu da kiraye-kirayensu,
ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko
don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama
haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima;
zai kāre ta ya kuma fanshe ta,
zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa. Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
“Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba;
takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye.
Za su gudu daga takobi
za a kuma sa samarinsu aikin dole.
Kagararsu za tă fāɗi saboda razana;
da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,”
in ji Ubangiji,
wanda wutarsa tana a Sihiyona,
wanda matoyarsa tana a Urushalima.