5
Waƙar Debora
A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
“Sa’ad da ’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora,
sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu,
suna yabon Ubangiji!
 
“Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki!
Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa;
zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
 
 
“Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir,
sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom,
ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo,
gizagizai sun zubo da ruwa.
Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai,
a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
 
“A zamanin Shamgar ɗan Anat,
a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi;
matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
Rayuwar ƙauye* a Isra’ila ta daina,
ta daina sai da ni, Debora, na taso,
na taso mahaifiya a Isra’ila.
Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli,
sai ga yaƙi a ƙofofin birnin,
ba a kuwa ga garkuwa ko māshi
a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
Zuciyata tana tare da ’ya’yan sarakunan Isra’ila,
tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
 
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna,
kuna zama a sirdin barguna,
da ku da kuke tafiya a kan hanya,
ku kula 11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye.
Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji,
ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila.
 
“Sa’an nan mutanen Ubangiji
suka gangara zuwa ƙofofin birni.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora!
Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa!
Ka farka, ya Barak!
Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
 
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari
suka sauko zuwa wajen shugabanni;
mutane na Ubangiji
suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne;
Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka.
Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro,
daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora;
I, Issakar yana tare da Barak,
yana binsa a guje zuwa kwari.
A yankunan Ruben
aka kuma bincike zuciya sosai.
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani
don ku ji makiyaya suna kiran garkuna?
A yankunan Ruben
aka yi bincike zuciya sosai.
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun.
Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa?
Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku
ya kasance a wuraren zamansa.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu;
haka ma Naftali a bakin dāgā.
 
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi;
sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi
a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo,
amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
20 Daga sama taurari suka yi faɗa,
daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
21 Kogin Kishon ya kwashe su,
tsohon kogi, kogin Kishon.
Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula,
suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’
‘Ka la’anci mutanensa sosai,
domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba,
su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
 
 
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel
matar Heber Bakene,
mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara;
a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti,
da hannunta na dama ta ɗauko guduma.
Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa,
ta ragargaza ta huda kunnensa.
27 A ƙafafunta ya fāɗi,
ya fāɗi; a can ya kwanta.
A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi;
a can ya fāɗi, matacce.
 
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa;
a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu,
‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba?
Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
29 Mafi hikima cikin ’yan matanta suka amsa mata,
tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba,
yarinya guda ko biyu wa kowane mutum,
riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera,
riguna masu ado,
riguna masu ado sosai don wuyata,
dukan wannan a matsayin ganima?’
 
 
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji!
Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana
sa’ad da ta fito da ƙarfinta.”
Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
* 5:7 Ko kuwa Jarumawa