4
Shugabanni da gwamnonin Solomon
Sai Sarki Solomon ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila.
 
Waɗannan su ne manyan shugabanninsa.
 
Azariya ɗan Zadok shi ne firist;
Elihoref da Ahiya, ’ya’yan Shisha maza, su ne marubuta.
Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne mai lura da takardu.
Benahiya ɗan Yehohiyada, shi ne shugaban mayaƙa.
Zadok da Abiyatar, su ne firistoci.
Azariya ɗan Natan, shi ne mai lura da shugabannin yanki.
Zabud ɗan Natan, shi ne firist da kuma mai wa sarki shawara.
Ahishar, shi ne sarkin fada.
Adoniram ɗan Abda, shi ne mai lura da aikin gandu.
 
Solomon yana da gwamnoni yankuna goma sha biyu a bisa dukan Isra’ila, waɗanda suke tanaji abinci domin sarki da kuma gidan sarauta. Kowanne yakan tanada abinci na wata ɗaya a shekara.
 
Ga sunayensu,
 
Ben-Hur, shi ne a ƙasar tudun Efraim;
Ben-Deker, shi ne a Makaz, Sha’albim, Bet-Shemesh da Elon Bet-Hanan;
10 Ben-Hesed, shi ne a Arubbot (Soko da dukan ƙasar Hefer);
11 Ben-Abinadab, shi ne a Nafot Dor (ya auri Tafat ’yar Solomon);
12 Ba’ana ɗan Ahilud, shi ne a Ta’anak da Megiddo, da kuma dukan Bet-Sheyan biye da Zaretan ƙasa da Yezireyel, daga Bet-Sheyan zuwa Abel-Mehola a ƙetaren Yokmeyam;
13 Ben-Geber, shi ne a Ramot Gileyad (Mazaunan Yayir ɗan Manasse a Gileyad suna a ƙarƙashinsa, haka ma yankin Argob a Bashan tare da manyan biranen sittin masu katanga da suke da ƙyamare na tagulla);
14 Ahinadab ɗan Iddo, shi ne a Mahanayim;
15 Ahimawaz, shi ne a Naftali (ya auri Basemat ’yar Solomon);
16 Ba’ana ɗan Hushai, shi ne a Asher da Bayelot;
17 Yehoshafat ɗan Faruwa, shi ne a Issakar;
18 Shimeyi ɗan Ela, shi ne a Benyamin;
19 Geber ɗan Uri, shi ne a Gileyad (ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da kuma Og sarkin Bashan). Shi ne kaɗai gwamna a bisa yankin.
Tanajin Solomon na kowace rana
20 Mutanen Yahuda da na Isra’ila sun yi yawa sai ka ce yashi a bakin teku. Suka ci, suka sha, suka kuma yi farin ciki. 21 Solomon kuwa ya yi mulki a bisa dukan masarautai daga Kogi* zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar. Waɗannan ƙasashe sun yi ta kawo haraji, suka kuma zama bayin Solomon dukan kwanakin ransa.
22 Tanajin Solomon na kowace rana su ne, garwa talatin na garin abinci, 23 shanun da aka yi kiwo a gida guda goma, shanu ashirin da suka ƙoshi daga kiwo, tumaki da awaki ɗari; ban da ƙishimai, bareyi, batsiyoyi, da kaji masu ƙiba. 24 Gama ya yi mulki a bisa dukan masarautai yamma da Kogi, daga Tifsa zuwa Gaza, aka kuwa sami zaman lafiya a kowane gefe. 25 A kwanakin da Solomon yake raye, Yahuda da Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba, sun zauna lafiya, kowane mutum ya zauna a ƙarƙashin itacen inabi da na ɓaurensa.
26 Solomon yana da rumfunan dawakai masu jan kekunan yaƙi, dubu huɗu, da kuma dawakai dubu goma sha biyu
27 Shugabannin yankuna, kowanne a watansa yakan yi tanajin abinci domin Sarki Solomon da kuma duk wanda ya zo teburin sarki. Sun tabbatar ba a rasa kome ba. 28 Kowa a cikinsu, bisa ga lokacin da aka ba shi, yakan kai hatsin sha’ir da ciyawa domin dawakan-kekunan yaƙi, da sauran dawakai a inda aka ajiye su.
Hikimar Solomon
29 Allah ya ba Solomon hikima da hangen nesa mai girma, da kuma fāɗin fahimta marar iyaka, kamar yashi a bakin teku. 30 Hikimar Solomon ta fi hikimar mutanen Gabas, ta kuma fi dukan hikimar Masar girma. 31 Ya fi kowane mutum hikima, har da Etan dangin Ezra ma. Yana da hikima fiye da Heman, Kalkol da Darda, ’ya’yan Mahol maza. Sunansa ya bazu ko’ina a ƙasashen da suke kewaye. 32 Ya yi karin magana dubu uku. Waƙoƙinsa kuwa sun kai dubu ɗaya da biyar. 33 Ya yi magana a kan rayuwar itatuwa, daga al’ul na Lebanon zuwa hizzob da yake girma a bangaye. Ya kuma yi koyarwa game da dabbobi, da tsuntsaye, da abubuwa masu rarrafe, da kuma kifi. 34 Mutane suka yi ta zuwa daga ƙasashe dabam-dabam don su ji hikimar Solomon. Sarakuna daga ko’ina a duniya, sun ji labarin hikimarsa, suka kuma aika da mutane don su ji shi.
* 4:21 Wato, Yuferites; haka ma a aya 24. 4:26 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na Seftuwajin (dubi kuma 2Tar 9.25); Ibraniyanci na da arba’in 4:26 Ko kuwa masu hawa