60
Ɗaukakar Sihiyona
“Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo,
ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
Duba, duhu ya rufe duniya
duhu mai kauri kuma yana bisa mutane,
amma Ubangiji ya taso a kanki
ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
Al’ummai za su zo wurin haskenki,
sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
 
“Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke.
Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;
’ya’yanki maza daga nesa,
ana kuma ɗaukan ’ya’yanki mata a hannu.
Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka
zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki;
za a kawo miki wadata daga tekuna,
za a kawo miki arzikin al’ummai.
Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar,
ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa.
Daga Sheba kuma duka za su zo,
suna ɗauke da zinariya da turare
suna shelar yabon Ubangiji.
Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki
ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima;
za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki,
zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
 
“Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai,
kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni;
jiragen Tarshish kuma su ne a gaba,
suna kawo ’ya’yanki maza daga nesa,
tare da azurfa da zinariya,
domin su girmama Ubangiji Allahnki,
Mai Tsarkin nan na Isra’ila,
gama ya cika ki da daraja.
 
 
10 “Baƙi za su sāke gina katangarki,
sarakunansu kuma za su yi miki hidima.
Ko da yake a cikin fushi na buge ki,
da tagomashi zan yi miki jinƙai.
11 Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe,
ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba,
saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai,
sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
12 Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka;
za tă lalace sarai.
 
13 “Darajar Lebanon za tă zo wurinki,
itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka
za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki;
zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
14 ’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki;
dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki
su kuma ce da ke Birnin Ubangiji,
Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
 
15 “Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki,
har babu wani da ya ratsa a cikinki,
zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama
da kuma farin cikin dukan zamanai.
16 Za ki sha madarar al’ummai
a kuma shayar da ke da nonon sarauta.
Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki,
Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
17 A maimakon tagulla zan kawo zinariya,
azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe.
A maimakon katako zan kawo tagulla,
baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu.
Zan sa salama ta zama gwamnarki
adalci kuma mai mulkinki.
18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba,
balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki,
amma za ki kira katangarki Ceto
ƙofofinki kuma Yabo.
19 Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba,
balle hasken wata ya haskaka a kanki,
gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki,
Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
20 Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba
watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba;
Ubangiji zai zama madawwamin haskenki,
kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
21 Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci
za su kuma mallaki ƙasar har abada.
Su ne reshen da na shuka,
aikin hannuwana,
don nuna darajata.
22 Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu,
ƙarami zai zama al’umma mai girma.
Ni ne Ubangiji,
cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”