Zabura 27
Ta Dawuda.
Ubangiji ne haskena da cetona,
wa zan ji tsoro?
Ubangiji ne mafakar raina,
wane ne zan ji tsoro?
 
Sa’ad da mugaye suka tasar mini
don su cinye ni,
sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari,
sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni,
zuciyata ba za tă ji tsoro ba;
ko da yake ya ɓarke a kaina,
duk da haka zan ƙarfafa.
 
Abu guda na roƙi Ubangiji,
wannan shi ne na nema,
cewa in zauna a gidan Ubangiji
dukan kwanakin raina,
in dubi kyan Ubangiji
in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
Gama a lokacin wahala,
zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa;
zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa
ya kuma sa ni can a bisa dutse.
 
Sa’an nan kaina zai ɗaukaka
a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni;
a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki;
zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
 
Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji;
ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!”
Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni,
kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi;
kai ne ka kasance mai taimakona.
Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni,
Ya Allah Mai cetona.
10 Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni,
Ubangiji zai karɓe ni.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji;
ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya
saboda masu danne ni.
12 Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina,
gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina,
suna numfasa tashin hankali.
 
13 Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa
zan ga alherin Ubangiji;
a ƙasar masu rai.
14 Ka dogara ga Ubangiji,
ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya
ka kuma dogara ga Ubangiji.