Zabura 3
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom.
Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne!
Su nawa suke gāba da ni!
Da yawa suna magana a kaina suna cewa,
“Allah ba zai cece shi ba.”
Sela
*
 
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji;
ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi,
ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki.
Sela
 
Na kwanta na yi barci;
na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
Ba zan ji tsoro ko dubu goma
suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
 
Ka tashi Ya Ubangiji!
Ka cece ni, ya Allahna!
Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi;
ka kakkarya haƙoran mugaye.
 
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo.
Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka.
Sela
* Zabura 3:2 Kalmar da ba a tabbatar da ma’anarta ba, mai bayyana sau da sau a cikin Zabura; mai yiwuwa kalma ce ta kiɗi.